Mujallarhausa.com.ng mujallarhausa










Mujallarhausa.com.ng

Home Hausa Novels| Sabbin Hausa Novels Sirrin Android Addini Hausa fim Fitattun Labarai Hausa Novels Downloads Kannywood MTN Music-Promoted Labarai wasanni

 

Wednesday, May 15, 2019

Download Tarkon Kauna Episode Arewa24

Download Tarkon Kauna Episode 57 Arewa24

Sunday, February 17, 2019

FARILLAN SALLAH FARILLAN ALWALA DA SUNONINTA


*FARILLAN ALWALA *

Farillan alwala guda 7 neh:

• Niyya

• Wanke Fuska

• Wanke hannaye zuwa gwiwar hannu

• Shafar kai

• Wanke kafafuwa

• Cuccudawa

• Gaggautawa

*SUNNONIN ALWALA*

• Wanke hannaye zuwa wuyan hannu

• Kurkure baki

• Shaka ruwa

• Fyacewa

• Juyo da shafar kai

• Shafar kunnuwa

• Sabunta ruwa agaresu

• Jeranta tsakanin farillah

*MUSTAHABBAN ALWALA*

• Yin bismillah

• Goga asuwaki

• Kari akan wankewa ta farko a fuska da

hannaye

• Farawa daga goshi

• Jeranta sunnoni

• Qaranta ruwa a nisa gabobi

• Gabatar da dama kafin hau.

*AKAN FASALIN ALWALA*

• Wanda ya manta da wata farilla daga gabobinsa, idan ya tuno sai ya aikata ta da

abunda ke bayanta, idan kuma yayi nisa sai ya aikata ta ita kadai, ya kuma sake abunda ya sallata bayan faruwar abun.

• Idan kuma ya bar sunna, to saiya aikata ta ita kadai bazai sake sallah ba.

• Wanda kuma ya mance lam'a sai ya wanke ta ita kadai da niyya, in kuma har yayi sallah by an faruwar hakan toh sai ya sake ta

• Wanda ya tuna da kurkurar baki ko shaqa Aruwa bayan ya rigaya ya fara wanke fuska, to bazai dawo gare su ba har sai ya gama alwalarsa, sannan sai yayi su

• Tsettsefe 'yan yatsu hannuwa yana wajaba, an so a tsettsefe 'yan yatsun qafafuwa, tsefe gemu mara dubu yana wajaba acikin alwala, tsefe gemu yana wajaba acikin wanka koh da mai duhu neh.

*AKAN FASALIN ALWALA (2)*

• Babu yana halatta ga wanda bashi da alwala yayi sallah, koh dawafi, koh ya taba al qur'ani koda acikin gafakarsa neh, bada hannunsa ba saidai idan *juzu'i* neh ga mai neman ilimi acikinsa.

• Yaro a wajen taba al qur'ani kamar babba yake, amma laifin yana wuyan wanda ya bashi al qur'anin ya taba.

• Wanda yayi sallah da gangan ba tare da alwala ba toh shi kafiri neh. Allah ya ki ya she mu.

*ABUBUWA MASU WARWARE ALWALA*

*_Karrai da Sababai_*

*Karrai sune:*

• Fitsari

• Bayan gida

• War rihu (tusa)

• Maziyyi

• Wadiyyi

*Sababai sune:*

• Bacci mai nauyi

• Suma

• Farfadiya

• Marisa

• Maye

• Hauka

• Sumbata

• Shafar mace, idan anyi da niyyar jindadi ko kuma ya samu jindadin babu nufi  Shafar azzakarinsa da cikin hannu ko da cikin yan yatsu duk ta warware.

°Wanda yayi ko kwanto acikin samuwar kari to alwala ta wajaba agareshi, saidai in mai yawan waswasi neh, to babu komai agareshi. Yana wajaba agareshi ya wanke dukkanin azzakarinsa saboda fitowar maziyy. Shi maziyy wani ruwa ne da yake fitowa lokacin 'yar sha'awa karama, ta yin tunani koh kallo koh yin wanin wannan.

*BAYANIN TSARKI*

_tsarki kashi 2 neh:_ °Tsarkin kari Tsarkin dau'da

• Dukkan su basa inganta saida ruwa mai tsarki, mai tsarkakewa shine: wanda kamarsa bata jirkita ba, ko dandanon sa, ko qamshinsa, da abunda yake rarrabe shi marinjayi. Babu laifi da kasar gishiri da kasar kanwa da makamancinsa.

• Idan najasa ta fito fili sai a wanke gurin, idanta fantsama sai a wanke tufar gabadaya.Wanda yayi kokwanto acikin samuwar najasa, to sai yayi yayyafi da ruwa ajikin kayan.

• Idan kuma wani abu ya sameshi sai yayi kokwanto acikin najastuwarsa, to ba sai yayi yayyafi ba.

• Wanda kuma ya tuna da najasa yana cikin sallah sai ya yanke sallar, saidai idan yaji tsoron fitar lokaci. Wanda yayi sallah da ita yana mai mantuwa sai ya tuna bayan yayi sallama to ya sake sallah idan da lokaci. Allah ya karbi Ibadunmu ya sa mu cika da Imani Ya kai dan uwa mai Albarka ka taya mu yada wannan karatu/sako zaka samu lada mai yawa, domin yada ilimi yana da daga cikin Abubuwan da suke kusan ta bawa ga Mahalicci.

Saturday, February 16, 2019

HAUSA NOVEL IN SO CHUTANE NA 1


*Godiya ga Allahu (S.W.T) mai kowa mai komai da ya bani ikon fara wnn novel cikin koshin lafiya.*

*Alhamdulillah Hamdan katheeran d'ayyiban mubarakan fiih.*


*Fatan alkhairi gareku masoya aduk inda kuke ,ku ke bani kwarin gwiwa ako wani lokaci nagode kwarai da gaske Allah ya bar k'auna.*


****** ***** *****


Da d'add'aya suke fitowa, dan zuwa ganin Wannan mai sa'a da ya sace zuciyar yayarsu har ta fita ta saurareshi. 


Ba ma fitar ne yafi basu mamaki ba, sai jimawar da tayi wajen zance daga cewa bari Inga waye ne in dawo. 


Kanwarta mai bi mata Nusaiba,wacce kusan kansu d'aya ita ta fara zuwa ta gaisheshi, sai Fati, itama taje da sunan taje gaisheshi, daga nan sai kannenta maza Nafi 'u da Hamza .


D'an autansu khalil ne kawai baije ba .dan shi d'an ba ruwana ne.

Gulma ajali. 

Hhhh gulma harda maza. 


Abinne kam da mamaki dan ko Mamansu da suke kira da Ummi ma cikin mamaki take fitar 'yar tata da rashin Dawowarta da wuri.


 Ummussalma kenan 'ya ga Mal. Abdullahi. 

Mahaifin Ummussalma Babban malami ne wanda yake karantar da manyan mutane da matasa. 

Har islamiyya na musamman ya bud'e kusa da gidanshi dan koyar da yaranshi da na makwabta. 


Cikin ikon Allah islamiyyar ta hab'aka har daga wasu anguwanni zuwa karatu akeyi .


Ummussalma wacce aka fi kira da Salma, kunnenta kuma suke ce mata Aunty Salma, itace 'ya ta uku a wajen iyayenta amma itace mace babba a gidan. 

Yayyunta biyu maza ne Allah yayi wa d'ayan rasuwa Saura d'aya wadda suke kira da Ya Al-amin. Wani lokaci su ce mishi yayanmu.


Tun tasowar ta tashi da burin ta zamo likita, ita kuwa a rayuwarta babu abinda yake burgeta irin taga nurses sanye da fararen kayannan Suna bawa mara lafiya taimako. 


Sosae take son karatu dan ita a rayuwarta babu abinda ya fiye mata karatunta muhimmanci. 


Tun gamawanta secondary school mahaifinta yaso ya aurar da ita amma ganin yadda ta nace kan karatu kuma bata da wani tsayayye dan ita Sam bata sauraron samari dan a ganinta b'ata lokaci ne, kuma hakan zai iya hanata karatunta yadda takeso. 


Babban abinda take gudu shine, kada babanta yasan tana da wani yace zai mata aure. 

Shi yasa Shima babannata ya hakura da batun aurar da ita kuma ya nema mata karatu a school of nursing.


Karatu take ba wasa dan samin cikar burin ta, kuma cikin ikon Allah tana samun nasara dan tunda ta fara bata tab'a samun matsala da karatun ba. 


Duk yadda wasu suke nuna mata Suna son ta, wasu ta hanyar kannenta suke bi,wasu kuma ta wajen yayanta wasu kam direct wajen Mal. Suke zuwa da bukatarsu ta aurenta, saidai yace musu sameta Su daidaita kansu dan shikam alk'awari ya daukarwa kanshi bazaiyiwa 'yarshi auren dole ba, ko wacce zai bata dama ta zab'i wanda takeso, nashi dai yayi bincike ne idan an dace da nagari Falillahil hamdu. 

Idan kuma akasin haka ne sai ya bata shawarar da zai amfaneta sai kuma ya bisu da addu'a. 


Samun ta a daidaitan shine matsalar dan ko kad'an bata bada fiskar da za'a kawo mata irin wnn maganar ta soyayya. 

Ko yaya mutum yaso tunkarar ta sai abin ya gagara dan Allah ya bata baiwar k'warjini, ga uwa uba d'aure fiska da takeyi idan ta fita waje, ko da mutum yayi dauriya da k'arfin halin yi mata magana ma daga kallon da Zata maka zaka San babu nasara ,gata kullum cikin zumbuleliyar hijabi ,zaiyi wuya Kaga dariyarta shi yasa Yawancin mutane suke ganin zata yi wayar shaani. 


itakam haka yafi mata Dan babu wanda zai kawo mata cikas a Karatunta.


Kannenta ,Nusaiba da Fatima duk suna da masu zuwa wajensu, fatimar nema Salma take hanata fita a cewarta idan auren takeso ma ta bari sai ta K'are secondary school. 

Itama Nusaiba dan ta K'are ne.


Wani lokaci haushi suke bata idan taji Suna maganar soyayya, ko kuma idan aka ce wani yazo wajensu taga suna rawan Kai. 


Yawancin mutane Suna gani girman kai ke damunta ko kuma dan taga tana da kyau yasa takeyin  hakan wasu kuma cewa suke mai kud'i take son ta aura. 


Saidai abin mamakin masu kud'in ma ba sauraransu takeyi ba. 

Abinda basu sani bama shine ita Sam a tsarinta bata son auren mai kud'i dan gani take auren mai kud'i sawa Kai damuwa ne. 

Na farko gani take kamar baza ta samu attention d'inshi yadda ya kamata ba.


Ta iya yiyuwa ta zamo kamar abokiyar gabar danginshi dan zasu sa mata ido sosae ganin d'an uwansu na da kud'i. 


Gani take shi dinma zai ga kamar dan kudinshi takesonshi ba dan Allah ba. 


Shi yasa take da burin idan Zata yi aure ta auri talaka d'an uwanta mai rufin asiri wanda kuma zai barta tayi aikin asibiti su zauna lafiya su rufawa juna asiri.


Thursday, February 7, 2019

NATSANE SHI NA 9 HAUSA NOVEL




NATSANE SHI NA 9 HAUSA NOVEL

[Dan iska ne]


WATTPAD ASMASANEE


بسم الله الرحمن الرحيم


9


Rawar sanyi jikin ta keyi tana lumshe idon ta da suka canza kala tsabar sanyin da take ji amma koh dar baiji tausayin ta ba hadde yadda take jirkice jirkice tana motsi,


Saima tafiya da yake slow down ya kuna wakar sa dake tashi slow yana tukin sa cike da Nisha di,


Daidai cikin harabar hotel din yayi parking,kmr ta san lkc da xai iso ta fito sanye cikin hourglass figure 8 off to d shoulder wiggle dress with sleeve wadda bata ida kai mata kasa ba sai karamin veil da ta azama kanta hannu ta rike da latest iPhone 


Ba tare da komi ta bude kofar wadda yayi daidai da vomiting dinda ya turnuke mufeeda with out any solution ta saki she da mugun karfi wadda yasa ya xuba a jikin iftinan da tayi tsaye speechless tana kallon yadda mufeeda ke xabga aman


Oh Allah wat is dis?wat are doing like dis iftinan tafada kmr xatayi kuka ga wata kalan kyankyami da tayi wiping saman fuskar ta ,


Saida ta kare vomiting din ta koma ta jin gina da kujerar tana maida numfashi,


Bude motar yayi ya fito inda iftanan ke tsaye tana wani kakkamewa tsabar yadda take jin jikin ta 


Follow me yafada yanayi gaba she don't have any choice she have to follow him yasa tabi bayan sa 


Simple gown ya suka saya ,sai da suka dauke one room ,saida tayi wanka ta canxa kaya dey spend almost to 1h a wurin,


Fitowa sukayi hannu su sarkafe acikin na juna,kmr wasu couple, Gyale ta tayi using ta goge bakin ta da inda ta fa ta na jikin ta,,sosai jikin ta ya sake 


Ita ta bude kofar gaba wadda yasa mufeeda dake bacci ya fixge ta saurin bude idon ta ta sauke saman nasu da suka aza mata na mujiya


Da sauri ta dauke nata,,,oya go back yafada yana kara jawo iftinan jikin sa,hk will even better for her,hakan yasa ta sauko tafito ta koma baya kwanciya tayi ta runtse idon ta tana jin wani irin bad feeling,,


Duk da halin da take ciki bai hana ta tsine masa ba ba adadi,


Driving yake suna fira da iftinan duk da duk yawon firar iftanan ce keyi daga uhm sai A'a daga karshe ma alama yayi mata da tayi shiru,


"Bakin gate din gidan yayi parking tun bai ida parking ba take kokarin bude motar,taji ta lock dole sai da ta hkr har yayi parking duk da ba kallon sa takeyi ba ama jikin ta ya bata harar ta yakeyi,lock din ya cire wadda yasa ta saurin bude motar ta fita tana tan gadi,


Kallon ta take looking her infinity har ta kasa dauke idon kn yadda taga tana tp she is totally speechless wacece ita ta tambaye kanta,wani numfashi ta sauke ,,tana so ta tambaye MUZFY saide halin shi ta sani tana iya tmbyr sa abun ya bare musu hkn yasa ta kama bakin ta tayi shiru,,,hr suka iso wani plat guest house wadda ya tsaru iya tsaruwa,


"Daker ta iya kai kanta part dinsu don akwai jayawa sosai kowa yayi bacci kmr ba gidan biki ba don yanxu hk past 2 direct bedroom dinta tafada saman bed ta saki matsanan cin kuka tana maiyi wa MUZFY Allah ya isa ba adadi,ks wanka tayi sai na'urar heater mai saka daki dumi ta kunna,ta cire kayan cikin ta ta saka nighty,tayi kwanciya taja duvet ta rufe hr kanta,,


*****Da karfe 2 na ranar lahadi akayi budar kai wanda ya tsaru iya tsaruwa anyi al'ada sosai a cikin sa da dare koh wace amarya aka sadata da dakin ta sai fatan xaman lpy,,


HEMU ne xaune gaban iyayen sa hadda ammy dake gefe tana sauraren nasihar da mijin nata kema danna su,sai take ji kmr MUZAFFAR ne akeyiwa amma ina ita bata taba jin MUZAFFAR yayi mgnr aure bakin sa,,,wani abun taji ya tsaya mata azuciya,


Daga karshe inaso kayi min biyayya Ibrahim kada ka duba auren hadi aka yi mk da muneera ka wulakan ta ta ,koh bada aure ba muneera yar uwar kace IBRAHIM kada kaci amanar xumunci daga karshe ina mai maka fatar alkhairi,Allah ya baku xuri'a dayibba,Allah yayi muku Albarka,,


Ameen su ka amsa gaba daya ummie sai famar doka murmushi take,, Gdy yayi musu yafita jikin sa a matukar sanyaye,,


Part dinda ya xamo mamallakin sa a yanxu ya nufa ,tsaruwa part din ya tsaru ba karya anarke dukiya 


Wane bedroom da yake gefe ya nufa ,gsk koshi kansa dakin ya burge shi duk da ba wani tarka ce aka xuba masa ba,


Wallpaper dakin kadai abun kallon ce balle ma aje ga royal family bed dinda aka shirga,,,


Kayan jikin sa ya rage ya fada toilet yayi wanka yayi wanka ya dauro alwalla jallabiya ya saka yayi raka a biyu yana naimar ma kansa xabin da yafi xama alkhairi gare shi,

"Jallabiya ya xare ya saka kayan bacci ya kashe wutar daki ya kwanta ,idan ya tuna da mgn dad yakanji yanayi na daban,a yanxu yana ji xaiyi xaman aure da muneera koh don farin ciki iyayen su,da hk bacci mai cike da nishadi ya dauke shi,,

Baccin sa koh hour biyu baiyi ba yaji ana knocking da dan karfi yajiya cikin baccin sa wadda yasa shi saurin bude idon sa mmk yake wanene hk da wannan daren 


Tashi yayi ya bude kofar sanye take cikin rosessence lace panty gown wadda iya kart kneel dinta , fuskar nan tayi shafe shafe da hawaye,


Da wani irin salo tafada jikin sa wadda yayi sanadiyar hadewar kirjin su wuri daya ta saka wane irin kuka tana goga kirjin ta a jikin sa,


Cikin kukan take fadin tsoro nake ji Hamma,ks tabuka komi yayi sai shafa mata baya yake alamar is ok,,


Jan ta yayi don su xauna Amma duk wada yaso ta rabe ajikin sa ki tayi hk yasa dole ya kwanta da ita a jikin sa yana mai tsintar kansa cikin yanayin da bai taba tsintar kansa a cikin ba,,


Duk yadda yaso ya kwace ga abunda xuciyar sa ke rayama sa kasawa yayi yadda muneera ke kara shige masa jiki , tsintar kansa yayi da sanya bakin sa cikin nata,,,


"Sosai ya shiga juya ta son ransa saide kam muneera bb ga.... Saide duk da hk yaji dadin kasancewa da ita ya kuma ji dd yadda ya same ta,,ba laifi 


********

Haka sauran amaren hk ta kasan ce a gefe koh wannen su don ba wadda gwarzon nata ya sarara mata,,,


"Mufeeda tun ranar asabar rabon ta da fitowa cikin site dinsu ba gidan amaryar da taje,duk hanyar da tasan xata ga MUZAFFAR bata bi,,

Kwata kwata bai damu da ita ba ya kan manta ta ajikin jerin wa'inda ya sani harakar gaban sa yakeyi cike da miskilanci,shirye shiryen komawar sa yakeyi Canada 


"Fitowar ta parlour kenan ta iske hassenat da hanna suna kallo,hanna na rike da big size din ice_cream tana sha,tunda ta kalle robar ice_cream din taji ranta ya biya(kanta ammy ta hana a saka ice cream cikin fridge din gidan)


Kusa da kanwar ta ta xauna sweet baby sis kallo akeyi hk mufeeda tafada tana sakar wa hanna murmushi,


Hanna najin sunan da ta kira ta dashi tasan ice cream din take so yasa itama ta sakar mata murmushi tace ya Nahar ,will u drink?Hanna ta tambaya da sauri ta daga kai alamar eh 


Gaba daya ta mika mata robar tace u can drink it all am ok with it inji hanna gyada mata kai mufeeda tayi alamar gamsuwa, Nan tafara shan ice cream din hkl kwance,,


Hanna..!!! Hanna..!! Hammad yake kwalawa twin sis din tasa kira Na'am my brox come am here at the parlour ta amsa masa 


Oya give me my ice cream dat brox brought fo...kasa ida mgn yayi ganin yadda mufeeda ta sarka fe teke tauri,daker ya tsaya mata ,kallo hanna tayi tace who brought dis ice cream for u?brox MUZAFFAR tabata amsa atakaice,,


Kuma kika bani Nahar ta tambaye Hanna still tana saka hannu ta cikin bakin ta don ta jawo tayi vomit Wat is there don na baki sis nd u are d one dat said I should give u miye laifi na?


Wani saka dan yatsanta tayi wadda yasa ta jawo vomit da karfi da gudu tafada toilet tana kwarara amai gaba dayan su da Ido suka bita suna tambayar kansu me hk ke nufi...?Gaba daya sai da ta kwarara abinda ke cikin ta ,sa'an tayi brush,


Damn it tayaya xa'ayi taci abinci koh abin sha da yafito ga hannu mazinaci never in life tafada a fili mgnr bata dira ga kunne kowa ba sai kunne MUZFY wadda fitowar sa kenan daga part din dad,,,

Wednesday, February 6, 2019

HAUSA NOVEL YARIMA ASMIN



HAUSA NOVEL YARIMA ASMIN

🅿59&60

Hannunta cikin nasa suka isa,zaune suka sami ammi kan kujera tana Jan tasbaha kuyanginta na gefenta.

"Tunda suka shigo idonta ke kan yasmeen har suka gaisa", tana tunanin meyasa take irin wannan tafiyar.

      Muryar yarimace takatseta yana cewa ammi zanje office in had'a duk wasu shaidu gobe zamushiga kotu..

(kasancewar yyiwa ammi bayanin komai)

Cikin jin dad'in har yanzun yana akan gsky tace to ALLAH yabada sa'a, yakaimu yatsaremun kai aduk inda kake..ameen yace yana murmushi.

       " kallon yasmeen yyi yace baby natafi..cikin jin kunya ta ce adawo lfy "fita yyi dukda yaso tarakasa gun mota amma bayaso ammi ta fahimci wani abu.,,,

Bayan yafita ,ammi takalli yasmeen tace oh yau duk kinyi shiru shiru kamar marar lfy, ko wani abu ke damunki ta kafeta da ido,azuciyarta tana cewa ALLAH yasa cikine da ita..

Yasmeen tace ah ah bb komai."

"Ahankali ammi tace jiya wani abu na auratayya yashiga tsakaninki da son?"

Kai aduk'e yasmeen tace eh.

Batace komaiba ta nufi bed room dinta, azuciyarta tana tausayin yasmeen dan tagane cewa yarima yana da fitina,toilet ta shige da kanta ta had'a ruwan dumi had'e da wasu magunguna sannan tazo ta ja hannun yasmeen ,bbu musu tabita..

      adede toilet din ammi ta tsaya had'e da cewa yasmeen kishiga aruwan dumin karki fito saisunyi sanyi..

To tace ta shige toilet din.,,,

Ammi kuwa kafin yasmeen ta fito harta had'a mata wasu magunguna da damesu da madara,tana fitowa tabata tace maza shanye kinji y'ata bbu musu ta shanye duka,ammi tace to kwanta kiyi bacci kinji,cikin jin dadi yasmeen tayi kwanciyarta kan bed din ammi me rumfa na gargajiya irin na sarauta,bbu jimawa bacci Yy gaba da ita Dan da ma bata samu bacci sosaiba jiya..


      ******


Yarima kuwa duk wasu shaidu nasa yarigada yahadasu ,bayan yagama komai yakira umman yasmeen bayan sun gaisa yace mata gobe ne Shari'ar da karfe10:am.

To tace had'e da sanar da shi aiga umar nanma yadawo jiya da dare dan yanaso ayi shara'ar yananan..


Yarima yace umma inbbu damuwa inaso yazo yanxun yasameni a office dina dama bamusan junaba,cikin jin dadi umma tace to ,sukayi sallama..


Yarima befi20 minit dayin waya da ummaba yah Omar yyi knocking,yarima yace yes nan yah Omar yashigo da sallama..


"" cikin sakin fuska yarima yatarbesa ,kallo d'aya yyi masa yagane shi jinin yasmeen ne".


Bayan yah Omar yyiwa yarima jaje nan yasake masa godiya akan k'okarinsa akansu,murmushi yarima yyi yace bbu komai yiwa Kaine.


ahankali yah Omar yace ina yasmeen sarkin shagwaba Nasan kana fama da ita da rigimarta...


Yar dariya yarima yyi yace oh baby Ashe kodai agd ba umma kadai takewa rigimaba harda kai,murmushi yah Omar yyi,azuciyarsa yace shima baby yake cemata kenan.nan yahau basa labarin yasmeen da yadda ya shagwaba.,,,


Ahankali yarima ce Ashe Kaine ka shagwabar da ita kenan,murmushi yah Omar yyi bece komai ba.


"Yarima yakalli agogon dke d'aure atsintsiyar hannunsa yacewa yah Omar muje muyi sallah ko?" Saimutafi gd Ku gaisa da yasmeen dan intaji kazo har office dina bakaje guntaba saitayi kusa kuka.""


Nan suka mik'e ,sai firarsu suke,kamar dama sun San juna bbu wani jida kai ko isa da yarima yanunawa Omar,shikanshi yah Omar din yaji dadi sosai kuma yana mamakin wai shine yau zaishiga gidan Sarki.


       ********

6angaren yasmeen kuwa ,bata farkaba sai 1:00pm da yan mintina,wasai taji jikinta ga tafiyarta ta daidaita.


"Part dinsu ta wuce tayi sallah ta gyara part din yarima,sannan tayi wanka had'e da yin wata fitinanniyar kwalli tasaka pink lass Riga da sket yyi masifar karbarta .


A waiting parlour ta zauna tana jiran yarima yadawo suyi lunch dan jiyane suka fara cin abinci tare sai yau dasukayi break jitake inbatare dashiba bazaci abinciba...sallamar su Maryam da salim ce ta katse mata tunani..


Zaunawa sukayi suna fira abinsu suna dariya...sallamar yarima yasmeen taji juyowa tayi ta ga yabude mata hannuwansa da gudu taje tafad'a jikinsa ,suna dariya itadashi..


Sama yad'aga ta yana juyi da ita ...bata auneba taji muryar yy Omar dinta yana oh ni yah Ashman agaba ake soyewar? ,da sauri ta kalli gefen..


Ido 4sukayi da yah Omar, ihun murna tasaki,had'e da cewa yarima yayah saukeni...da gudu ta fad'a jikin yah Omar tana murna..,,


Maryam kuwa suman zaune tayi ganin wannan kyakkyawan santalelen saurayin,masha ALLAH take cewa azuciyarta dama wannan ne yah Omar din da yasmeen keyawan fadi' aibatayi zaton yawaye hakab...muryar yarima taji yace keeeeee!baki iya gaida mutaneba?


kallon gefen da yah Omar yake tayi cikin class tace ina wuni?Shikuwa yah Omar lumshe ido yyi jin sweet voice dinta ,yace lfy atakaice dan kallo daya yyimata yaji ta tafi da imaninsa

Tuesday, February 5, 2019

HAUSA NOVEL YARIMA ASHMAN NA 56

HAUSA NOVEL YARIMA ASHMAN NA 56

Story & written by mujallarhausa.com. ng


🅿55&56

6angaren su yasmeen kuwa afusace yarima yajata suka isa bed room d'insa. Kan bed yafad'a had'e da kwanciya rigingine yalumshe idonsa yanajin zafin abinda Anty lubnah tayiwa yasmeen.

"yasmeen dke kallonsa dan ta lura ransa yabaci sosai",

Kan k'irjinsa ta kwanta .

         " ahankali tace pls kayi hkuri ",hannu yasa yashafi gashinta yace ,bazan taba barin wani ya wulak'antaki ba keda familynki  agabana ,inkyale dole nad'au mataki...wayarsa ce tayi ringing

Janye yasmeen yyi dg jikin sa yanufi gun mirror yadauki wayar dan me martaba ne ,jinayi yace yanxun?to ganinan xuwa,kashe wayar yyi yabude sif d'in kayansa yafito da suit bakak'e ,kallon yasmeen yyi yace baby xoki shiryani.

     " tasowa tayi fuska bbu walwala tace yaya ina zakaje?"

Kallonta yyi yace abbane yakirani naje governor da shugaban alk'alai nason mgn dani yanxun..

"batace komaiba " saidai sai wani d'aure fuska take tana turo baki gaba, tata yasa yashirya ,tayi saurin juyawa dan tafiya ..da sauri yarima yarik'e  hannunta,yajanyota jikinsa.

"Ahankali yace baby nah menene?"

Fad'amun kinji?turo baki tayi,saiga hawaye sharrrrr afuskarta,subhanallahi, yarima yace had'e da janta kan bed ya azata kan cinyarsa ,yanaso su had'a ido amma tak'i yarda.

Murya k'asa k'asa yace pls kifad'amun mekikeso?

"cikin kissa da Jan hankali tace nibanaso katafi kabarni ", kada asaceka.

Murmushi yyi yace oh baby rigima ,insha ALLAH lfy zandawo ai kina mun addua keda amminah kada kidamu kinji babyn yayanta...

Cikin shagwaba ta ce to muje tare.

       Ware ido yyi cikin rarrashi yace kizauna gun ammi nadawo akwai maza agun bazai yuyu mujeba...ihun da yasmeen tasaka yasashi yin shiru ,sai kukan shagwaba take ita bazai tafiba,da k'yar yashawo kanta tayi shiru ,yayi mata rollyn da mayafinta yaja hannunta zuwa gun ammi,amma azuciyarsa mamakin kansa yake wai yau yarima shine ke rarrashin mace,shinmeyasa bayasan  ganin ta tana kuka?meyasa yakeson abinda takeso,...hannunsa da yasmeen ta girgiza yasashi dawowa tunaninsa wasu tanuna masa sukayi masa jaje,sannan suka Shiga ciki.,,,,


Ammice a parlourn da kuyanginta ,suna ganin su yarima suka fita,murmushi ammi tayi tace oh my son sai ina kuma?


" nan ya sanar da ita gun dazashi "


Yasmeen ta kalla taga kamar tayi kuka,tunawa tayi da abinda lubna tayi msta k'ila shiyasa tayi kuka....muryar yarima ta ji yace ammi ga baby nan ki lallabamun ita nadawo sai koke koke takeyi wai kada asake saceni..


"Murmushi ammi tayi tace oh, xonan y'ata kinji yadawo,ai ALLAH yana tare da shi gakuma adduarki datawa kinji."


Zama yasmeen tayi gefen ammi,shikuwa yarima kasa tafiya yyi ,duk'awa yyi yayiwa yasmeen rad'a jinayi tace da gske yaya? yace eh ,dariya sukayi shida ita,itadai ammi na gefe dan ita aganinta summa manta tana gun ,tashi yasmeen tayi tace muje narakaka yaya...


,,,kafin yarima yyi mgn ,umman yasmeen tayi sallama da gudu yasmeen taje ta fad'a jikinta tana ihun murna.,,


Murmushi yarima yyi yace oh baby nidai kada kikayarmun da ummanah.


Umma cikin fara'a tace gskiyarka kuwa dan haryanxun tak'i girma..hararan yarima yasmeen tayi ta kalli ammi dkema umma maraba tace ammi kingansa ko yana Jana..


Yar dariya ammi tayi tace ALLAH ka kiyayeni,..murmushi yarima yyi yatsugunnah suka gaisa da Umma tamasa jaje,tukum yatafi...


Umma  kuwa bayan sun gama gaisa wa da ammi tamata jaje ,sannan yasmeen tajata wai tazo part dinta su gaisa,datak'i xuwa Saida ammi tasaka baki tukum tabita suka tafi.


Bayan sun sake gaisawa,umma ta fito da na u,rar da yarima yabata (takunna in bala yaje gdnta)


"Yasmeen tace name ne umma?"


Umma tace ki aje in mijinki yadawo kibasa,kinji ki Adana,nan tace to.


Cikin jin dad'in ganin yasmeen tana cikin kwanciyar hankali da zaman lfy da mijinta da danginsa ,taitawa yasmeen nasiha had'e da cemata ai Omar yace gobe zaidawo Nigeria dan ayi komai agaban idonsa.


Yasmeen tace ,aisai yahuta tukum sannan afara shariar,amma umma kina ganin da saka hannun Kawu a mutuwar abbanmu?


Umma tace hmmm yasmeen kenan,inmijinki yadawo kinji tabakinsa Nina tafi,jiki ba kwari tayiwa umma rakkiya tadawo part dinta ta shige bath room dan yin wanka..



      ***********

bangaren yarima kuwa koda yafita tare da Sarki had'e da security, suka nufi gidan Governor aka tattauna mgnar su waye sukayi kiddinapping dinsa?


Bbu boye boye yarima yyi ma governor da shugaban alk'alai bayanin farkon Shari arsu dakawu bala da alhj jamilu, sbd yasmeen ne,Yakima sanar dasu irin kamun dayyiwa alhj jamilu da yara 2zaisace.

         sannan yasanardasu zargin da akewa bala akan shine yakashe mahaifin yasmeen.

"nan aka aje magana tunda suna hannun hukuma to kawai ashiga kotu tunda akwai shedu ayi shara'a akan abinda ake zarginsu."

Maganar kiddinapping akyalesu kawai...sai in anyanke musu hukunci asaka su fito da sauran mutanan da su aikata kiddinapping din tare..

Badan yarima yasoba ya amince da hakan had'e da cewa jibi xa'a fara shariar zuwa gobe zai had'a shaidunsa...

Bayan sun fito ,yarima yacewa Sarki zai wuce police station, nan kowa yyi gun dazashi,dukda yarima bai waniso security suka biyosaba to dan dai Sarki yace subisane shiyasa...


Suna isa dpo yabashi ghanonin da aka kamasu da kud'i aciki,umarni yarima yyi da asaka kudin a boot .


Yarima yace akaisa gun da bash yake,bbu musu ,suka kaisa...


"Hmmmm duk Wanda yaga bash saiya tausaya masa yyi bak'i kirin yarame yafita kamanninsa sbd wahala da horo mai tsanani,ammafa da alama yahorun..


,,yana ganin yarima yazube yana tuba da Neman afuwa yasaka asakesa.,,


" shima yarima yalura da yashiryu yagane rayuwa,dan haka yace asakesa."


dg gun bash ,sell din dasu ahj jamilu suke yarima yanufa..kwance magashiyan yasamesu sunci duka na fitar hankali ,duk fuskokinsu akumbure,dan inba saninsu kayiba bazaka ganesuba,dan duk ancanja musu kamanni da dukan da'aka musu..


""" kalon tsana yarima yabisu dashi had'e da tafa hannuwansa ,yace sannunku masu iya dubara ,Ashe a iyanan wayonku yatsaya hmmmm inaso kusani jibi Ku shirya shiga kotu dan duk inda kukai wadanda kuka kashe kuma zakubisu...bala dan kunya kasa d'aga kansa yyi shikuwa ahj jamilu sai tsinewa bala yake wai shine yasakashi aikata hakan.


Tsaki yarima yyi yace ai kiddanapping nawa da kukayi shima bazan kyalekuba zan d'auki mataki Ku azatonku ,k'arshenku bazaizoba,hmmm kunyi kuskure.


Nasan kunyi mamakin yadda nagane June kukamun haka,sbd kunsaka safar fuska ko?


To bari kuji ko sau d'aya naji muryar mutum indai mugune to zanganeshi aduk inda naji muryar shi,yana fadin haka ya kalli dpo yace acigaba da azabatardasu su fad'i inda sauran mugayen suke akamosu. Dpo yace to, nan yarima yyi tafiyarsa.


Bank suka nufa suka mayar da kudin tukum suka dawo gida ,alokacin anata Kiran magrib,masjid ya wuce be fitoba Saida akayi isha'i..


da kansa yaja mota yaje yasiyawa yasmeen nama gashashshe da ice cream, sannan yanufo gd.


bayan ya iso part din yasmeen yaje batacan,nasa yaje canma batanan ledojin dayazo dasu ya aje kan bed yawuce part din ammi.



Tafiya yake azuciyarsa yana jin haushin miyasa bazata jirasaba matsayinsa na mijinta sai dai shi yaje yakirata wato ita bata damu dashiba kenan..


"Tsaki yyi yashige parlourn ammi ,aikuwa tana can ,gaida ammi yyi had'e da cewa yasmeen yauwa,tana cema sannu da xuwa..


Kallon ammi yyi yace Saida safe ya fita..


Tab'e baki yasmeen tayi had'e da mikewa ,sukayi sallama da ammi ,tana tunanin lfy tagansa yana wani shan k'amshi da tunanin ta fita .


Jitayi anrungumeta ta baya,cikin shagwaba ta ce ,nika cikani sai wani d'aure fuska kakemun agaban ammi kana wani basarwa shine yanxun zaka wani r...rufe mata baki yyi da hannunsa yace muje sarkin shagwaba aikece wai bazakijiraniba sainaje natafi dke kin kyauta?


Ji yasmeen tayi batasan Bacon ransa,cikin sanyin murya tace to Yayana nabari,murmushi yyi yace ko kefa har naji dad'i muje ki karbi tsarabarki danamiki,bbu musu tabisa part din sa.


Bed room dinsa suka Shiga....




Wednesday, January 30, 2019

Yan Nigeria- Hattara Martaba da darajar Buhari da kuke gani dodo-rido ce ___Obasanjo

Yan Nigeria- Hattara Martaba da darajar Buhari da kuke gani dodo-rido ce  ___Obasanjo

Olusegun Obasanjo ya bada tabbacin cewa Alhaji Atiku Abubakar, shi ne zai lashe zaben shugaban kasa mai zuwa domin ya cire kasar daga cikinkuncin da Take ciki  Obasanjo ya ce martaba da darajar da jama'a ke kallo a jikin shugaban kasa 


Muhammadu Buhari dodo-rido ce  Ya ce ya yafewa Atiku Abubakar akan dukkanin wasu laifuka da ya yi masa, yana mai cewa ya soke duk wata yarjejeniya ko taimakekeniya da ya kulla da Buhari a baya Tsohon shugaban kasa Olusegun

Obasanjo ya bada tabbacin cewa dan Takarar shugaban kasa karkashin Jam'iyyar PDP, Alhaji Atiku Abubakar, shi ne zai lashe zaben shugaban kasa na Ranar 16 ga watan Fabreru, saboda shine mutumin da ya dace ya cire kasar Daga cikin halin kuncin da take ciki.

Da ya ke jawabi a ranar Laraba a wani Taron lakca da aka shirya kan harkokin kasuwanci na Island Clube 2019 da ya gudana a birnin Legas, Obasanjo ya ce martaba da darajar da jama'a ke kallo a Jikin shugaban kasa Muhammadu

Buhari dodo-rido ce, yana mai cewa dukkanin matakan da shugaban kasar ke dauka na tabbatar da rashin dattakonsa. Obasanjo ya ce ya yafewa Atiku Abubakar akan dukkanin wasu laifuka da ya yi masa, yana mai cewa ya soke duk wata yarjejeniya ko taimakekeniya da ya kulla da Buhari a baya

Kalli hotunan Maryam Yahaya

Kalli wasu kaya tattun hotunan Maryam Yahaya


Jarumar fina-finan Hausa, Maryam Yahaya kenan a wadannan hotunan nata da ta haskaka, ta sha kyau, tubarkallah, muna mata fatan Alheri

Dada mujallarhausa.com.ng

Tuesday, January 29, 2019

Macen Farko Mai Digirin Digirgir A Fannin Shari'ar Musulunci --AMINA DIYALLO


Mace Ta Farko 'Yar Kasar Guinea Da Ta Samu Digirin Digigir A Fannin Shari'ar Musulunci A Fadin Kasar Guinea Baki Daya MADALLAH DAGA WWW.MUJALLARHAUSA.COM.NG

Download [Video] Dadin Kowa Sabon Salo Episode 88


DOWNLOAD


Domin kallon cigaban shirin dadin kowa na satinda ya wuce ku kasance damu. ACIKIN WANNANSATIN:- Kawai ku biyomu domin ganin yaddazata kasance a cikin shirin. Asha kallo lafiya

yar kwalisa kalli wasu zafafan hounan BILKISU SHEMA

F

Fitacciyar Jarumar Kannywood wadda Kowa yafi saninta Da Bilkisu Shema Tace kullum mu kasance Cikin Godiyar Allah Alhamdulillah Ala Kulli Haal DAGA WWW.MUJALLARHAUSA.COM.NG