AUREN FARI 34mujallarhausa.com.ngMujallarhausa.com.ng mujallarhausa










Home Hausa Novels| Sabbin Hausa Novels Sirrin Android Addini Hausa fim Fitattun Labarai Hausa Novels Downloads Kannywood MTN Music-Promoted Labarai wasanni

Sunday, January 27, 2019

Home › › AUREN FARI 34

Subscribe Our Channel




AUREN FARI 34

......... Ta zumburo baki.

Ya kalleta da kyau bazakije ba ne ko kuwa Dubai din ke bakya so?. Ki fadi kasar da kike so umaimah you have that right.

  Ni ba tafiyar ke bana so ba zolayar nan ta jirgi idan zai tashi nake tsoro wallahi hanjin cikina kamar zasu fito........ Har kwanciya yayi saboda dariya ta yi murmushi wallahi ka fiye mugunta kai kuwa.

  Sai da yayi mai isar sa sannan ya ce ba irin wancen jirgi zamu hau ba, wannan na daban ne sha kurumin ki wifee.

   Ta ce *Hmmm*

Ki matso muci ko na kamoki yanzu nayi miki dura,..... Ta matso da sauri saboda tasan duk abinda madaki ya ce zai yi to zai iya, suna ci yana janta da fira.

   Wayar sa tayi kara, gaban sa yayi mummunan faduwa ganin sunan samira, ya dauka idan ta gane mace ce ya shiga uku, ya ki dauka shima matsala.

  Ta dan saci kallon sa ganin waya nata ringing har tana niyyar katsewa, ya dan bata fuska ya daga yana kallon fuskar ta..... Hello Aunty har kun isa?

   Samira ta dauke wayar daga kunnen ta tayi saurin kallon screen din tana zargin ko ba *Madaki* ta kira ba,

  Yaji shiru, yaci gaba da cewa amin na gode Aunty Allah yabar zumunci ya latse wayar. Dai dai ta mayar da ita kunne itama.

  Toooo faa! Ta fada tana zaro ido, wai ya akayi? Ta mike tsaye, lallai abinsa azimun ne wannan yarinyar tsoron ta yakeyi kamar rai da ajali. Abinda yafi na shafa ma kaina lafiya da *Matashin yaro* idan ya nemeni welcome idan bai nemeni ba kuma umma ta gaida asshhaa ina dalili.

  Ya kalleta tana ta tura dankalin da kyar sai kawai ya sha mur, ke juyo ki fuskance ni.

  Gabanta ya dan fadi ta juyo tana kallon sa kanta a kasa,

   Na lura sai na biyo miki ta bayan gida sannan zamu shirya ko? Kin dai san yanda mukayi jiya da ke ko?

Ta daga kai *Eh*

To ina nan akan baka na babu abinda zan miki, sai dai dole ki sauarara kin kindaya miki sharudda saboda yanda na ke kokarin tsara zaman namu bazai taba tafiya dai dai ba.

  Kin dai San yanzu ke matata ce ko? Ta daga kai *Eh*

Good to bazan jure wannan makurewar ba wallahi kinji na rantse. Na farko anan zan kwana yau nida ke saman gadon can...... Ta zaro ido wallahi na tuba zan yi yanda kake so.......... Jira da Allah malama, kawo man ke akayi in kalla? Na ce ba abinda zan miki kin kuma San abinda nake nufi da hakan sai dai bazan iya hakurin wannan makurewar ba, idan kin hana in taba ki baya yanzu dai baki da iko.

   Magana ta biyu zaki ringa bani abinci daga yanzu a baki har in koshi, sannan ba maganar zama nesa dani ko kusa dani kin ga nan? Ya bugi cinyar sa nan ne mazaunin ki Allah. ......zatayi magana ya daga mata hannu *umarni nake baki* ba wai ina neman shawarar ki ba.

 Tayi narai narai, sai magana ta uku idan ina barci zaki tasheni dole kema ki kwanta kusa dani kina shafani a hankali kina kiran sunana har na farka ko kin gane?

   Ta daga kai *Eh*

Good taso ki dawo nan toh ya janyo hannunta , tayi sukutii ....ya kalleta wallahi ki ware kawai don baki ga komai ba game da dokokina ba.

  Ta fara debo dankalin zata bashi ya ce hajiya ajiye chokalin da hannu ake ba mai gida abinci........

  Na bani kawai.....ta fada azuci.

Da ta bashi ta kara debowa sai ya rike hannun ranki ya dade ba a sauri *Slowly*........ Ya kashe mata ido.

 Ta yi dai sukuy, yana koshi ya gyara zama sannan ya rungumeta kamar jaririya yana bata, ( yau na ga ta kaina ni umaimah ) ta fada kamar ta nutse.

     Karfe biyu ya shirya ya ce mata zai je cikin gari.

  Tana fitowa ta kira su bilky ta kwashe bokitan gara duka ta ce a mayar sashen mamee hada manshanu.

   Tana ciki tana harhada kudin gudunmuwa bata san wainar da suke toyawa ba, umaimar ta shiga . Tana ganinta ta washe fuska 'yar halak yanzu nake tunanin ki a raina.

ta zauna tana tayata harhadawar mamah kuma ba sai ki kirani ba?

  Tayi dariya kawai, ashe gobe zaki kara katari da nutumen? Duk sukayi dariya sannan ta turo baki wallahi bana kaunar abinda ka kara hawa dani jirgi mamah ki ce a bar tafiyar don Allah.

   Uwani ina ni ina hana tafiyar da an gama komai gobe goben nan?, to ki shirya mu tafi tare don Allah mamah......... Ke bani son iyashege, haka kawai sai in biku?

  Ta langabe idanunta suka kawo ruwa wallahi zanfi jin dadi idan muka tafi da ke don ni tafiyar gaba daya bana so........ Ta ajiye kudin hannun ta kafin ta kamo hannuwanta duka biyun.

  Uwani ki kwantar da hankalinki ba abinda zai faru sai alkhairi, idan kuka tsaya garin nan tabbas ke kanki abin sai ya dameki saboda fitar nan da kika ga yayi office ya tafi, wallahi matukar madaki na garin nan bazai huta ba.

  Kuma kema dama ce gareki da zaki San me mijinki keso meye baya so........ Bata san lokacin da bakinta ya kucce ta ce humm ba.

   Bata bi ta kanta ba taci gaba da cewa, kuma kya gano gari kiyo kallo tunda naji yawo zakuyi kasashe don jirgi ai sabawa zakiyi wancen ma don karonki ne na farko.

  Ta fara janta da yar firarraki har ta dan saki.

Suna zaune falo ya shigo tara da rabi har ta gota, uwani da mamee ya fada yana murmushi, ina so inji yanda firar ku take kasancewa yanzu su uwani an zama matar madaki, 

  To rasa kunya beran tanka,zaka fara ko? 

Uwani tashi ki tafi daki kada ya hanaki sakewa kinji, tayi zumbur ta wuce simi simi ya bita da kallo iyye yarinya sama tayi yau bad akin mamee ba…….itama mikewa tayi ta wuce ciki, yana waigowa yaga har ta kusa shigewa y ace mamee ina zuwa? Ko waigowa batayi ba barci nake ji kasan akwai gajiya tayi ciki.

Ya danyi murmushi kai mamee karshe ce wallahi.

Tana ta kakkabe kakkabe tama rasa me zatayi hankalinta a tashe wai gado daya zata kwana da madaki. Ta yi kasa da murya ba abinda ke cikin aure sai fargaba, takura, zullumi da tsoro.

Wallahi kamar in gudu nakeji………….ki tafi ina?

Tayi firgigi ko kadan bata ji shigowar sa ba. Ta danyi kasa da kai, ya kamota zo nan meke tayar miki da hankali kike tunanin guduwa?

Ya bata rai umaimah dana san baki kaunata da ban aure ki ba…..Allah bah aka bane, to menene?

Tayi shiru, ya zauna bakin gado ita kuma ya dorata bisa cinyarsa, umaima wallahi aure da kike ganin sa babu abinda ke ciki sai jin dadi, farin ciki,walwala da nishadi. Shi yasa Allah SWA cikin suratul rum yake cewa : kuma na halitta maku matan aure sannan na sanya soyayya da nutsuwa a tsakanin ku lallai wannan ayar mutane ce masu yin tunani.

   Saboda haka ki saki jikin ki wallahi zan jiyar da ke dadin da ba’a taba jiyar da wata mace shi ba, zan shagwabaki yanda ake shagwaba yaro daya tilo wanda iyayensa suka samu bayan sun dade suna rokon haihuwa kuma daga shi basu karaba, zan kula da ke yanda duk baki tsammani na jiyar da ke dadin da ba kowa ce zata sameshi ba.

Abinda duk kike tsoro sai ya faru yau, gobe , jibi ,next month,next year ke any time but zai zo miki lokacin da baki tsammani lokacin da baki tsorona, lokacin da kika saba dani, lokacin da kika san dadin madaki…….. kawai ki saki jiki dani wannan shine abinda nake bukata umaimah saboda ni mutum ne mai son kula, kuma ina sha’awar taba jikin ki wanda baki isa ki hana ni ba duk tsoron ki duk wata makurewa da zakiyi.

Tun kafin in fara gwada miki karfi kawai ki ware hajia, ya tallao fuskar  ta. Ya harareta wallahi matukar baki rage wannan kunyar ba tabbas zan gaggawar wancakalar da ita a wuce wurin….

Kinji ko?

Ta daga kai tana murmushi.

Kilibabba irin ku kunfi jaraba sumimu kasau, ni yanzu gashi dai na karya record yau idan kinji wayoyin abokai dana amsa wani dan iska ma cewa yayi zai zo ya rakani in kaiki asibiti. Basu san cewar ni madaki ba haka nake ba lokacin da ake tunanin da zanyi abu sai na kiyi ko laifi akayi man lojkacin da ake tunanin zan dau mataki sai anyi shiru, wallahi umaimah sai kin zauna zaki fahimceni bani da fitina da kike ganina na mugun miskili ne ni kawai ke baaki gane bane saboda yanayin chakwakiyar mu ko kuwa? Duk suakayi dariya,

 ta ce wai chakwakiya, eh mana ko kin manta yakin da muka gabza kika farden hannu? Ya kyalkyace da dariya kai naga bala’I ni ummaru.

Tayi murmushi, ya mike ya fita sai gashi da gyalen hajia wanda ta bata aro lpkacin da suakyi ma juna wankan miya a fatin asma’u, ta fara tafa hannu tana salati, daman yana hannunaka? Ya yi murmushi ke wannan gyalen ai kusan haukatani yayi lokacin da muna cikin fitinar idan na dauko shi zuciyata har hayaki takeyi don azaba. Da kuwa na kamu da son ki da kin gudu kin barni sai na zo na daukeshi ina bege. Ta kyalkyace da dariya ta ce wai bege. 

    Nan da nan ta sake kawai suka hau fira hada tafawa, sai  kusan sha biyu ya watsa ruwa yayi yayi da kyar ta shiga kewaye ta janzo kayan barci wata guntuwar riga iya cinya fitowa ta gagara sai shine ya fiddota da tsiya tana hawa gado tayi saurin yayo bargo ta lullube , ya hawo yana taunar cingam…. Yarinyar nan wallahi da gangan akayi budurwar kauye ai ke sunan ya dace da.

Ya janyo ta zo kiga yanda ake barci da miji hancinsa da nata ya haduya matseta ganin zata zulle malama jira haba, ya kura mata ido kaii ya naga hancinci bai kai nawa tsawo ba lallai cewa zakiyi akwai ragi ga abinda na bayar…….. yayi dariya idan kunya kike ji rufe ido in miki kallon tsaf!! Ta rasa in da zata sanya kanta, ya kura ma dan bakinta ido, ALLAH sai nayi kissing…..ya ayyana azuci.

Ke bude kiga wani abu ….bude bude bude…….ya fada kamar ga ma abin nan ya taho gadan gadan… tayi saurin budewa ya fiddo cingam din bakinsa ungo kici…..tayi saurin runtse ido gashi ya riketa ta ce nag a ta kaina anya bawayau zai mun ba?......bata karasa tunani ba taji bakin sa cikin nata……wata kunnanniyar wuta ta dauke mata, ta rasa duniyar da take . yafi mintuna goma sai da yaji network na neman dauke mishi ya sa kawai ya zare a hankali. Ta tafi da kanta luuuuu ta soke cikin  kirjinsa ya maida hannuwansa bayanta ya rufe su da bargo ………………mu kwan lafiya. 

Na bakin madaki lallai umaimah anji network. Don sallar asubah ma sai da ya dawo masallaci sannan ya tada ta,

Ya tasa ta gaba ya dinga mata dariya wai taji network barci harda minshari. Ta yi ta hararar sa, dai taci gaba da lazimi. Da kansa ya hada masu kayayyakin da zasu tafi daasu cikin yar karamar jaka daya. Cikin ranta tace kilan jibi zamu dawo.

     Mamee bata koma ciki ba sai da taga fitar su gate, umaimah nata matsen kwalla duk tunaninta airport sukayi sai kawai taga sun dau hanyar gidan su. Wani dadi ya kumeta, musanman da ta hango baban tsaye kofar alamar isowar su yake jira.

Kafin ta fito kofar gidan ya cika da jama’a ta dan raba tayi gidan hajiya da sauri, gudu gudu ta fito har ya shiga mota yana jiranta, yana hangota ya fito ya isa wurin ta ya fakaici mutane ya saka mata kudi a jaka y ace bakauya idan mutane sun taru haka don kai alheri ake masu , tayi sukuti daman taga ya yi rabo cikin gida su luba har da rawa da taga umaimah.

Ta dan juya ta hango auwalu mai manja ta yahuto shi da hannu ta damka mishi daurin kudi ta ce raba muku tayi mota da sauri, suna dagawa ya kalleta yana dariya ina cewa zakibi kowa ne ki bashi.

Tayi yar dariya tabbb! Da sun karya ni kuwa……au ashe kin sani ta harareshi kawai.

   Suna zuwa jirgi na slow, ko zama basuyi ba ya cacumeta wa kike ma harara dazun, sukayi bisa doguwar kujera rikichaaaaa ya fara mata chakulkulo tun tana zullewa har ta fara kyalkyatar dariya tana zillewa…… ana haka yaji jirgin ya tashi har y agama saisaituwa sararin samaniya…. Ya dan saketa, tayi jimm tana gyara cucukuyar kayanta tana zullumin tashin jirgi sai kawai ta hango hazon gajimare, nan da nan ta fahimceshi.

Ya kwantar da ita jikin sa yana fadin dumaman jiki in dan runtsa please…………..Maman Abdallah.



No comments:
Write Comment